
Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Nasiru Sani a wannan mako ya tabo batun matsalar yawan sharar da jama'a ke zubarwa a gefen titunan garin Suleja na jihar Neja a Najeriya, inda shirin ya duba illar hakan da kuma matakan da ya kamata a dauke don magance matsalar.
Jan 7, 2023
19 min

Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Nasiru Sani ya mayar da hankali kan matsalar da manoman Najeriya ke fuskanta ta satar amfanin gona dai dai lokacin da wasu sassa na kasar ke fama da matsalar karancin zubar ruwan sama wanda ake alakantawa da sauyin yanayi.
Nov 19, 2022
20 min

Shirin namu a wannan makon, zai duba rahoton hadin-gwiwar kungiyoyin manoman Najeriya dake gargadi kan yawan amfanin gonar da ake sacewa musamman a gonakin arewacin kasar a daidai wannan lokacin na girbi, satar hatsin da rahoton ke cewa zai shafi girbin bana ta fannin karanci da tsadar cimmaka.
Oct 29, 2022
19 min

Shirin Muhallinka tare da Nasiru Sani ya duba yadda ta'ammali da miyagun kwayoyi ke taka rawa sosai wajen gurbata muhalliu, kamar yadda binciken masana ya tabbatar.
Oct 22, 2022
20 min

Shirin Muhallinka rayuwarka tare da Nasiru Sani ya dora kan makamancin shirin na Makon jiya da ya yi duba kan yadda Najeriya ta gaza mayar da hankali don cimma alkawurran da aka dauka karkashin Yarjejeniyar Malabo da ta bukaci sanya kashi 10 na kasafin kudin kasashen Afrika a fannonin aikin noma.
Sep 24, 2022
19 min

Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare Nasiiru Sani, kamar yadda aka saba ya kan tabo batutuwan da suka shafi Noma da Kiwo ko kuma sauyi da dumamar yanayi, inda a wannan makon shirin ya tabo taron masana harkokin Noma a Najeriya, game da yarjejeniyar Malabo da ta bukaci sanya kashi 10 na kasafin kudin kasashen Afrika a fannonin aikin noma.
Sep 10, 2022
20 min

Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Nasiru Sani a wannan mako ya mayar da hankali kan yadda kananan manoma ke fama da karancin takin zamani bisa zargin jami’an da gwamnati ke damkawa alhakin rarrabawa na karkata takin zuwa hanun yan baranda yanayin dake kara ta’azzara karanci da tsadar takin ga manoma.
Sep 3, 2022
19 min

Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Nasiru Sani da bisa al'ada ke yin duba kan Noma da kiwo ko kuma sauyi ko dumamar yanayi a wannan karo ya tabo yadda mahukuntan Najeriya suka hana amfani da wasu nau'ikan magungunan feshin amfanin gona da kuma shirin tsaftace sana'ar magungunan wanda masana suka gano cutarwarsu ga lafiyar jama'a.
Aug 27, 2022
20 min

Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Nasiru Sani a wannan mako ya mayar da hankali kan yanayin Damuna a jamhuriyyar Nijar musamman a jihar Maradi inda mahukunta suka fara bayar da kyautar takin zamani la'akari da tsadar takin wanda ke barazana ga yiwuwar fuskantar karancin cimaka a kasar.
Aug 20, 2022
19 min

Kasashen da dama a Afirka ta yamma da na Sahel za su fuskanci ruwan sama masu yawan gaske da ambaliya ,wannan hasashe daga masana na zuwa a dai-dai lokacin da ake kawo karshen taron hukumar kulla da yanayi na kasa a Najeriya Nimet a Abuja.Nasiru sani ya samu tattaunawa da masana dangane da wannan hasashe a cikin shirin Muhalinka rayuwarka daga Rfi.
Jul 24, 2022
20 min
Load more
